fidelitybank

Ta hanyar da ta dace shugaban Binance ya fice daga Najeriya – Makusancinsa

Date:

Amurka ta ce tana da masaniya a kan rahotannin tsare ɗanƙasarta a Abuja.

A watan da ya gabata ne aka kama shugaban kamfanin Binance, Tigran Gambaryan tare da abokin aikinsa, Nadeem Anjarwalla, wanda ke da fasfon Birtaniya da Kenya a wani ɓangare na binciken kaucewa biyan haraji da gwamnatin Najeriya ke yi wa kamfanin na kuɗin kirifto.

Mai magana da yawun ofishin jakadancin Amurka a Najeriya, ya shaida wa BBC cewa, “A duk lokacin da aka samu wata matsala ta tsare ɗanƙasarsu a wata ƙasa, to ofishin jakadancin da ke ƙasar na yin duk mai yiwuwa wajen bayar da taimakon da ya dace.”

Ofishin jakadancin ya ƙi bayar da cikakken bayanai game da tsare ɗanƙasar, yana mai cewa saboda dalilai na sirri.

Yanzu haka Nadeem Anjarwalla, ba ya hannun Najeriya bayan da mahukuntan ƙasar suka tabbatar da cewa ya tsere, to amma wata majiya daga makusantansa ta ce ya bar Najeriya ne ta hanyar da ta dace.

Mahukuntan Najeriya dai sun ce suna aiki da jami’an tsaro don samar da takardar sammaci ga Mr Anjarwalla.

A ɓangare guda kuma, mahukuntan Najeriya sun maka kamfanin a gaban kotu inda suka shigar da tuhume-tuhume da suka shafi ƙin biyan haraji. In ji rahoton BBC.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp