Rohatanni nanu ni da cewa, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince tsohon gwamna, Abdullahi Adamu ya karbi rikon jamâiyyar APC.
Wata majiya mai karfi har daga fadar wasu gwamnoni ta shaidawa Daily Trust cewa, Muhammadu Buhari ya nuna ya na tare da Sanata Adamu.
Shugaban Buhari ya nuna inda ya karkata ne a wajen taron da ya yi da gwamnonin APC a Aso Villa. Amma babu mamaki Abdullahi Adamu ya fuskanci adawa daga wasu masu neman wannan kujera da ake ta hange tun bayan sauke Adams Oshiomhole.
Wani gwamna ya ce shugaban kasa ya ce shugaban jamâiyya zai fito ne daga Arewa ta tsakiya, kuma Adamu ya cancanta, kuma babu wanda ya yi masa gardama.