fidelitybank

Taƙaddama ta ɓarke tsakanin APC da PDP a kan miƙa mulki

Date:

Taƙaddama ta ƙaure tsakanin gwamnatin APC mai barin gado da kuma ta jam’iyyar PDP mai zuwa a jihar Zamfara, bayan zargin cewa ƙananan kwamitocin karɓar mulki na gwamati mai jiran gado na wuce gona da iri.

Gwamnatin jihar ta yi zargin cewa ƙananan kwamitocin na zuwa ma’aikatun gwamnati suna yin bincike tare da karɓar bayanai, wanda a cewar ta abu ne da bai dace ba kuma ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki.

Gwamnatin APCn ta ce abubuwan da kwamitocin ke yi yi tamkar ‘kafa gwamnati ne a cikin wata gwamnati’, inda ta buƙaci da su jira har sai an miƙa musu mulki.

Kwamishinan yaɗa labaran jihar, Ibrahim Dosara, ya shaida wa BBC cewa ƙananan kwamitocin sun kasance suna bin ma’aikatu suna karɓar bayanai da gudanar da bincike tare da karɓar bayanan asussan ajiya na ma’aikatun domin yin bincike.

“Duk bayanai da ake buƙata, ma’aikatun sun tattara tare kuma da miƙa wa kwamitin bayar da mulki, inda za su bai wa gwamna mai ci wanda shi kuma zai kira gwamna mai shigowa su zauna inda zai miƙa masa bayanan,” in ji Dosara.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp