Tawagar Super Eagles ta Najeriya ta yi kasa da matsayi daya a jerin kasashen da FIFA ta fitar a watan Yuni, inda ta zama ta 31 a duniya kuma ta hudu a Afirka.
Bisa kididdigar da hukumar ta FIFA ta fitar a ranar Alhamis, ‘yan wasan da Jose Peseiro ya koyar sun samu maki 1,504.7 a cikin watan da ake nazari.
A matakin nahiyoyi kuwa, ita ce ta hudu bayan Senegal (18), Morocco (22) da Tunisia (30).