fidelitybank

Super Eagles ba za ta raina Guinea-Bissau ba – Osimhen

Date:

Dan wasan gaba na kungiyar Super Eagles, Victor Osimhen ya ce dole ne kungiyar ta tunkari wasanta na gaba da Guinea-Bissau a gasar cin kofin Afrika na 2023 da muradin samun nasara.

Osimhen ya dage cewa yana da kyau Super Eagles kada su raina mutanen Baciro Cande.

“Muna da burin samun kwarin guiwa a karawar da Guinea-Bissau. Babu shakka za su tunkari wasan da azama, kuma ba za mu raina kowace kungiya ba, idan aka yi la’akari da abin da suka yi na samun cancantar,” in ji Osimhen bayan wasan.

“Mun hadu da su a wasannin share fage kuma mun san karfinsu. Sun ci mu a gida, yayin da mu ma muka doke su.

“Don haka, muna sa ran za a yi wasa mai tsauri da su. Za mu yi iya kokarinmu don samun nasara.”

Super Eagles ta koma matsayi na biyu a rukunin A bayan da ta doke Cote d’Ivoire da ci 1-0 a ranar Alhamis.

Tawagar Jose Peseiro tana bukatar canjaras ne kawai daga wasan da suka yi da Guinea-Bissau domin samun gurbin zuwa zagaye na 16.

Za a yi karawar ne a filin wasa na Felix Houphouet Boigny da ke Abidjan ranar Litinin mai zuwa.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp