fidelitybank

Sulhu tsakani na da Wike gudun magana ne ba tsoro ba – Fubara

Date:

A yayin da ake ci gaba da takun-saka da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike da Gwamna Sim Fubara na Jihar Ribas, a yanzu haka gwamnan ya ce matakin da ya dauka na rungumar yarjejeniyar zaman lafiya da Shugaba Bola Tinubu ya kulla a tsakanin su, ba wai tsoro ba ne gudun magana ne kawai.

Fubara ya ce ya dauki matakin ne domin ganin an samu zaman lafiya a jihar.

Ya yi wannan jawabi ne a wajen liyafar da gwamnatinsa ta gudanar a gidan gwamnati da ke Fatakwal, kamar yadda wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Boniface Onyedi ya fitar.

Fubara ya ce gwamnatinsa ba za ta tsunduma cikin duk wani kazamin yakin siyasa da zai kawo cikas ga alkiblar ci gaba a jihar ba.

Ya ce, duk yarjejniyar da suka kulla ba don tsoro ba ne, amma saboda suna da muradin mutanen jihar, kuma suna girmama dattawa.

Fubara da Wike sun yi takun-saka kan tsarin siyasa a jihar Ribas.

Rikicin dai ya sa wasu ‘yan majalisar dokokin jihar suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, yayin da wasu kwamishinonin suka yi murabus.

Sai dai an soki Fubara da rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar saboda wasu sharuddan da ake zargin ba su amince da shi ba.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp