fidelitybank

Sugaban Sudan ta Kudu ya kai ziyara Rasha

Date:

Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir yana ziyara a birnin Moscow domin tattaunawa da shugaban ƙasar Rasha Vladimir Putin.

Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da Rasha da ƙasashen yammacin duniya ke ƙoƙarin neman goyon bayan ƙasashen Afirka bayan mamaye Ukraine.

Mr Kiir ya isa babban birnin ƙasar Rasha ne a ranar Laraba inda mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar Andrey Rudenko Yurevich ya tarbe shi, kamar yadda sanarwar fadar shugaban ƙasar ta bayyana.

Ofishin Mista Kiir ya ce ganawar da zai yi da shugaba Putin a ranar Alhamis, za ta tattauna kan batutuwan da suka shafi ci gaban dangantakar ƙasashen biyu a fannoni daban-daban.

Ta kara da cewa ziyarar na da nufin kara karfafa hulɗar diflomasiyya da kuma haɗin gwiwa a ɓangaren ciniki da zuba jari da kuma tsaro.

Sanarwar ta kara da cewa shugabannin biyu za su tattauna batun ɗage takunkumin hana sayar da makamai da kuma takunkumin da aka kakaba wa wasu mutane a Sudan ta Kudu.

A watan Mayun da ya gabata ne dai Rasha ta kaurace wa kuri’ar da kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi na sabunta takunkumin da aka kakaba wa Sudan ta Kudu, da suka haɗa da kwace kadarori da hana zirga-zirga da kuma sanya takunkumin makamai.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp