fidelitybank

Sufeton ‘yan sanda ya rasa ransa a hannun ‘yan ESN

Date:

Wasu da ake zargin ‘yan kungiyar tsaro ta Eastern Security Network, ESN,  da laifin kashe wani sufeton ‘yan sanda a ofishin ‘yan sanda na Ndiegoro da ke Aba, jihar Abia.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:30 na daren ranar Talata a hanyar Ohanku, mahadar Iheorji a garin Aba.

A lokacin da lamarin ya faru, ‘yan sanda sun kashe biyu daga cikin maharan a fafatawa da suka yi.

NAN ta bayyana cewa jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Abia, SP Geoffrey Ogbonna ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ogbonna ya ce, wasu ‘yan sanda daga ofishin ‘yan sanda na Ndiegoro suna sintiri a kewayen Iheorji lokacin da wasu da ake zargin ‘yan kungiyar ESN/IPOB ne suka kai musu hari.

“A yayin da aka yi musayar wuta da bindiga, daya daga cikin ‘yan sandan ya rasa ransa.

“Yayin da suka harbe dan sandan, sun kuma karbo bindigar AK-47 na ‘yan sanda,” in ji shi.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp