fidelitybank

Su El-Rufa’i ba za su taɓa kayar da Tinubu ba – Sule Lamiɗo

Date:

Tsohon gwamnan jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya danganta kalubalen da Najeriya ke fuskanta ga ‘yan kasar.

Da yake jawabi a gidansa da ke Bamaina a yayin bikin azumin watan Ramadan a ranar Lahadi, Lamido ya mayar da martani kan kiraye-kirayen kafa sabuwar jam’iyyar siyasa domin kalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.

Ya ce ’yan Najeriya sun yanke shawarar fitar da jam’iyyar People’s Democratic Party, PDP daga mulki, suka kawo APC ba tare da tunanin illar da hakan zai iya haifarwa ba.

“Kamar yadda na sha fada, ‘yan Najeriya ba su da masaniya game da Tinubu, kwararre ne kan yaudara da son kai,” in ji Lamido.

Kalaman nasa sun biyo bayan kiran da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi, inda ya bukaci jiga-jigan jam’iyyar adawa da su hada kai a karkashin jam’iyyar SDP domin ceto Najeriya daga hannun gwamnati mai ci.

Lamido, ya yi watsi da ra’ayin, yana mai cewa motsin rai da fushi kadai ba za su iya kayar da Shugaba Tinubu ba.

“Ba za ku iya kalubalanci Tinubu da fushi, kwadayi, ƙiyayya, hassada, ko mugunta ba, shi ne gwanin duk wannan,” in ji Lamido. “Manufar gaskiya da kishin kasa ne kawai za su iya fuskantarsa ​​yadda ya kamata.”

Ya kuma bukaci ‘yan siyasa da a da su PDP su dawo jam’iyyar, yana mai jaddada cewa babu kunya a sake haduwa da ‘yan siyasar da suka yi nasarar mulkin kasar nan a tsakanin 1999 zuwa 2015.

Ya kara da cewa “Lokacin da al’umma ke fuskantar matsaloli, shugabanninta kada su bari korafe-korafensu su shafi hukuncinsu.”

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp