fidelitybank

Su El-Rufa’i ba za su taɓa kayar da Tinubu ba – Sule Lamiɗo

Date:

Tsohon gwamnan jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya danganta kalubalen da Najeriya ke fuskanta ga ‘yan kasar.

Da yake jawabi a gidansa da ke Bamaina a yayin bikin azumin watan Ramadan a ranar Lahadi, Lamido ya mayar da martani kan kiraye-kirayen kafa sabuwar jam’iyyar siyasa domin kalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.

Ya ce ’yan Najeriya sun yanke shawarar fitar da jam’iyyar People’s Democratic Party, PDP daga mulki, suka kawo APC ba tare da tunanin illar da hakan zai iya haifarwa ba.

“Kamar yadda na sha fada, ‘yan Najeriya ba su da masaniya game da Tinubu, kwararre ne kan yaudara da son kai,” in ji Lamido.

Kalaman nasa sun biyo bayan kiran da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi, inda ya bukaci jiga-jigan jam’iyyar adawa da su hada kai a karkashin jam’iyyar SDP domin ceto Najeriya daga hannun gwamnati mai ci.

Lamido, ya yi watsi da ra’ayin, yana mai cewa motsin rai da fushi kadai ba za su iya kayar da Shugaba Tinubu ba.

“Ba za ku iya kalubalanci Tinubu da fushi, kwadayi, ƙiyayya, hassada, ko mugunta ba, shi ne gwanin duk wannan,” in ji Lamido. “Manufar gaskiya da kishin kasa ne kawai za su iya fuskantarsa ​​yadda ya kamata.”

Ya kuma bukaci ‘yan siyasa da a da su PDP su dawo jam’iyyar, yana mai jaddada cewa babu kunya a sake haduwa da ‘yan siyasar da suka yi nasarar mulkin kasar nan a tsakanin 1999 zuwa 2015.

Ya kara da cewa “Lokacin da al’umma ke fuskantar matsaloli, shugabanninta kada su bari korafe-korafensu su shafi hukuncinsu.”

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp