fidelitybank

Soludo bai ayyana tsawa takarar ta zarce ba a wa’adi na biyu ba – Gwamnatin Anambra

Date:

Kwamishinan yada labarai na jihar Anambra, Law Mefor, ya ce gwamnan jihar, Farfesa Chukwuma Soludo, bai bayyana aniyar tsayawa takara a karo na biyu ba.

Hakan dai ya sabawa rade-radin cewa Soludo na neman wa’adi na biyu a matsayin gwamna.

Mefor wanda ya zanta da manema labarai a ofishinsa a ranar Larabar da ta gabata, ya ce duk da cewa har yanzu gwamnan bai bayyana sake tsayawa takara a karo na biyu ba, za a shawo kan shi ya tsaya takara saboda bajintar da ya nuna.

Ya ce: “Soludo bai bayyana aniyar tsayawa takara a karo na biyu ba. Ya shagaltu da sanya manufofi a jihar don bunkasa jihar.

“Ina daya daga cikin wadanda za su sa shi ya tsaya takara, kuma idan ya yi takara, zan tabbatar ya yi nasara. Ya nuna kansa shi ne abin da mutanen Anambra suke so.

“Duk alamun suna son Soludo. Shi dan Anambra ta Kudu ne, kuma tsarin shiyya ya fifita shi. Tsarin shiyya-shiyya da muke da shi a Anambara shi ne mutum ya cancanci wa’adi na biyu.

“Idan Soludo ya fafata, na tabbata zai yi nasara domin ba zai gaya wa kowa cewa zai yi hakan ko ya yi hakan ba, gara ya nuna musu abin da ya yi.

“Soludo na da damar tsayawa takara karo na biyu. Masu cewa za su fafata da shi, su ne wadanda suka fafata da shi a lokacin da ba gwamna ba ne kuma ya ci su.

“Me ya sa kuke ganin ba zai sake lashe su ba, yanzu da yake da shaidar abin da ya yi wa mutanen Anambra?

“Soludo yana da tabbataccen nasarori, nagartattun nasarori a Anambra, kuma duk abin da ya kamata ya yi shi ne ya nuna wa mutanen Anambra katin sa don sake zabar sa a karo na biyu,” in ji Mefor.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp