Tsohon ministan wasanni, Solomon Dalung, ya fice daga jam’iyyar APC.
Dalung wanda ya rike mukamin minista a gwamnatin shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya mika wasikar ficewa daga jam’iyyar APC zuwa ga shugaban jam’iyyar na Unguwa da ke unguwar Sabon Gida a karamar hukumar Langtang ta Kudu a jihar Filato.
Wasikar mai kwanan wata 1 ga Afrilu, 2022, kuma dan siyasar ya sanya wa hannu a ranar 18 ga Afrilu, 2022. A cewar manema labarai.
Wani bangare na wasikar ya kara da cewa, “Wannan shi ne in bayyana ficewa ta daga jam’iyyar APC daga ranar da wannan sanarwar ta fito. In ji Dalung.