Jama’ar yankin Sabon Birni a Jihar Sokoto sun aike wa Shugaba Muhammadu Buhari, wasikar nuna bacin ransu a kan irin kisan gillar da ‘yan ta’adda ke yi musu kusan kullum a yankin.
Shugabannin karamar hukumar, sun aike wa Buhari wasikar ce bayan ’yan ta’adda sun kashe akalla mutum 80 cikin dare daya a Jihar Sokoto.
Kisan na biyu na zuwa ne bayan wasu ’yan ta’adda sun tare wata mota a kauyen Gidan Bawa da ke jihar, inda suka kone fasinjoji sama da 40 kurmus.
Wasikar ta bayyana wa Buhari takaicinsu kan irin kisan gillar da a a ke yi, musamman a yankunan Isa, Sabon Birni, Goronyo da kuma karamar hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara wadda ke makwabtaka da Jihar Sokoto.
Shugabannin yankin sun ce ’yan ta’adda masu biyayya ga kasungurmin dan bindigar nan, Bello Turji, na kai farmaki kan al’ummomin yankunan, inda suke yi wa mata fyade baya ga lalata dukiyoyin jama’a.
A baya jama’ar Sabon Birnin sun taba rubuta wa Shugaba Buhari wasika domin shaida masa irin mawuyacin halin da suke fuskanta a yankinsu.
Takaicin kisan gillar ya sa fusatattun mutane da zargin Buhari da rashin katabus a kan lamarin, sai ma tafiya Jihar Legas da ya yi a ranar Alhamis, domin halartar taron kaddamar da littafi.
Tuni dai mutane a kafafen sada zumunta suka shiga kira da a yi zanga-zanga tare da neman wa shugaba Buhari ya sauka daga mulki kan rashin kawo karshen matsalar tsaro da ta damu wasu yankuna, musamman na Arewacin Najeriya. Inji Aminiya.