fidelitybank

Sokoto: Mazauna Sabon Sara sun aike da wasikar baccin rai ga Buhari

Date:

Jama’ar yankin Sabon Birni a Jihar Sokoto sun aike wa Shugaba Muhammadu Buhari, wasikar nuna bacin ransu a kan irin kisan gillar da ‘yan ta’adda ke yi musu kusan kullum a yankin.

Shugabannin karamar hukumar, sun aike wa Buhari wasikar ce bayan ’yan ta’adda sun kashe akalla mutum 80 cikin dare daya a Jihar Sokoto.

Kisan na biyu na zuwa ne bayan wasu ’yan ta’adda sun tare wata mota a kauyen Gidan Bawa da ke jihar, inda suka kone fasinjoji sama da 40 kurmus.

Wasikar ta bayyana wa Buhari takaicinsu kan irin kisan gillar da a a ke yi, musamman a yankunan Isa, Sabon Birni, Goronyo da kuma karamar hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara wadda ke makwabtaka da Jihar Sokoto.

Shugabannin yankin sun ce ’yan ta’adda masu biyayya ga kasungurmin dan bindigar nan, Bello Turji, na kai farmaki kan al’ummomin yankunan, inda suke yi wa mata fyade baya ga lalata dukiyoyin jama’a.

A baya jama’ar Sabon Birnin sun taba rubuta wa Shugaba Buhari wasika domin shaida masa irin mawuyacin halin da suke fuskanta a yankinsu.

Takaicin kisan gillar ya sa fusatattun mutane da zargin Buhari da rashin katabus a kan lamarin, sai ma tafiya Jihar Legas da ya yi a ranar Alhamis, domin halartar taron kaddamar da littafi.

Tuni dai mutane a kafafen sada zumunta suka shiga kira da a yi zanga-zanga tare da neman wa shugaba Buhari ya sauka daga mulki kan rashin kawo karshen matsalar tsaro da ta damu wasu yankuna, musamman na Arewacin Najeriya. Inji Aminiya.

 

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp