fidelitybank

Sokoto: Mazauna Sabon Sara sun aike da wasikar baccin rai ga Buhari

Date:

Jama’ar yankin Sabon Birni a Jihar Sokoto sun aike wa Shugaba Muhammadu Buhari, wasikar nuna bacin ransu a kan irin kisan gillar da ‘yan ta’adda ke yi musu kusan kullum a yankin.

Shugabannin karamar hukumar, sun aike wa Buhari wasikar ce bayan ’yan ta’adda sun kashe akalla mutum 80 cikin dare daya a Jihar Sokoto.

Kisan na biyu na zuwa ne bayan wasu ’yan ta’adda sun tare wata mota a kauyen Gidan Bawa da ke jihar, inda suka kone fasinjoji sama da 40 kurmus.

Wasikar ta bayyana wa Buhari takaicinsu kan irin kisan gillar da a a ke yi, musamman a yankunan Isa, Sabon Birni, Goronyo da kuma karamar hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara wadda ke makwabtaka da Jihar Sokoto.

Shugabannin yankin sun ce ’yan ta’adda masu biyayya ga kasungurmin dan bindigar nan, Bello Turji, na kai farmaki kan al’ummomin yankunan, inda suke yi wa mata fyade baya ga lalata dukiyoyin jama’a.

A baya jama’ar Sabon Birnin sun taba rubuta wa Shugaba Buhari wasika domin shaida masa irin mawuyacin halin da suke fuskanta a yankinsu.

Takaicin kisan gillar ya sa fusatattun mutane da zargin Buhari da rashin katabus a kan lamarin, sai ma tafiya Jihar Legas da ya yi a ranar Alhamis, domin halartar taron kaddamar da littafi.

Tuni dai mutane a kafafen sada zumunta suka shiga kira da a yi zanga-zanga tare da neman wa shugaba Buhari ya sauka daga mulki kan rashin kawo karshen matsalar tsaro da ta damu wasu yankuna, musamman na Arewacin Najeriya. Inji Aminiya.

 

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp