fidelitybank

Sojojin sama sun yi lugudan wuta a maɓoyar Ƴan Boko Haram

Date:

Rundunar sojin sama ta ce, ta yi luguden wuta a kan mayakan da ta ce suna samun mafaka a Tumbun, yankunan da ke kusa da Tafkin Chadi a cikin jihar Borno.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, rundunar sojojin saman kasar ta ce jiragenta sun harba bama-bamai inda suka lalata maboyar wadanda ta kira ”yan ta’adda’ kuma ta tarwatsa sansaninsu.

Ta ce jiragenta sun kai hare-haren ne daga ranar 27 zuwa 30 ga watan Satumba, lokacin da aka tabbatar da ayyukan ‘yan ta’adda, masu barazana ga cibiyoyin sojoji da fararen hula da ke zaune a Tumbun Fulani da Tumbun Shitu, in ji sojin sama.

Sanarwar da daraktan hulda da jama’a na rundunar sojojin sama Air Commodore Edward Gabkwet ya fitar na cewa an ga mayaka suna dora jarkoki a cikin motocin a-kori-kura da ake girkawa bindigogi har guda biyu da aka boye a cikin tsirrai.

Bayan kai hare-haren ne, sojojin saman sun ce an kashe dumbin ‘yan ta’adda, sannan an lalata motocin.

Haka zalika, hare-haren da jiragen yaki suka kai a Tumbun Shitu bayan an gano maboyar bata-gari rufe a karkashin surkuki, inda kuma aka hangi motocin a-kori-kura uku da ake girka wa bindigogi suna shiga. Ta ce bayan an yi luguden wutar, rundunar ta yi bibiya inda ta tabbatar da hallaka ”yan ta’adda da dama da kuma lalata motocin a-kori-kura’.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...
X whatsapp