fidelitybank

Sojojin sama sun yi lugudan wuta a maɓoyar Ƴan Boko Haram

Date:

Rundunar sojin sama ta ce, ta yi luguden wuta a kan mayakan da ta ce suna samun mafaka a Tumbun, yankunan da ke kusa da Tafkin Chadi a cikin jihar Borno.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, rundunar sojojin saman kasar ta ce jiragenta sun harba bama-bamai inda suka lalata maboyar wadanda ta kira ”yan ta’adda’ kuma ta tarwatsa sansaninsu.

Ta ce jiragenta sun kai hare-haren ne daga ranar 27 zuwa 30 ga watan Satumba, lokacin da aka tabbatar da ayyukan ‘yan ta’adda, masu barazana ga cibiyoyin sojoji da fararen hula da ke zaune a Tumbun Fulani da Tumbun Shitu, in ji sojin sama.

Sanarwar da daraktan hulda da jama’a na rundunar sojojin sama Air Commodore Edward Gabkwet ya fitar na cewa an ga mayaka suna dora jarkoki a cikin motocin a-kori-kura da ake girkawa bindigogi har guda biyu da aka boye a cikin tsirrai.

Bayan kai hare-haren ne, sojojin saman sun ce an kashe dumbin ‘yan ta’adda, sannan an lalata motocin.

Haka zalika, hare-haren da jiragen yaki suka kai a Tumbun Shitu bayan an gano maboyar bata-gari rufe a karkashin surkuki, inda kuma aka hangi motocin a-kori-kura uku da ake girka wa bindigogi suna shiga. Ta ce bayan an yi luguden wutar, rundunar ta yi bibiya inda ta tabbatar da hallaka ”yan ta’adda da dama da kuma lalata motocin a-kori-kura’.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp