Rundunar sojin sama ta kasa da ke aiki a jihar Zamfara ta kashe wani shugaban ‘yan bindiga, wanda aka fi sani da Dogo Rabe da wasu ‘yan kungiyarsa sama da 45 a dazuzzukan Zamfara.
Jami’an rundunar sojin saman Najeriya sun yi ruwan bama-bamai a sansanonin ‘yan bindigar da ke tsakanin al’umomin Zurmi da Birnin Magaji a jihar Zamfara da Jibia a jihar Katsina, kamar yadda wata majiyar tsaro ta bayyana.
Kwanaki kadan kafin tashin bam din, an kai wani hari makamancin wannan a sansanin na wani sarkin ‘yan bindiga, Bello Turji da ke unguwar Fakai a jihar, inda aka kashe ‘yan bindiga a kalla 22, yayin da Turji ya tsere.
A cewar wata majiya daga yankin, Abdulbaqi Aliyu, harin na baya-bayan nan ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindiga a kalla 40 a yankin Birnin Magaji na jihar.
“Rundunar sojin saman Najeriya ta kai farmaki a dajin Sabon Birini Dan Ali, a karamar hukumar Birini Magaji, wanda ya yi sanadin kashe ‘yan fashin sama da 40,” inji shi.
An kai harin ne a lokacin da aka ce gungun na lodin shanun da aka sace.
“Ba a bayyana adadin mutanen da aka kashe a wannan farmakin ba saboda ‘yan bindigar sun taru a gidan Dan Karami domin yin taro. Babu tabbas ko yana cikin wadanda aka kashe,” inji majiyar.
Kawo yanzu dai babu wata sanarwa a hukumance daga Abdul Olaitan, kakakin rundunar sojin sama a jihar Katsina yayin da bai amsa kiran manema labarai ba.