fidelitybank

Sojojin sama sun kashe shugaban ‘yan bindiga a Zamfara

Date:

Rundunar sojin sama ta kasa da ke aiki a jihar Zamfara ta kashe wani shugaban ‘yan bindiga, wanda aka fi sani da Dogo Rabe da wasu ‘yan kungiyarsa sama da 45 a dazuzzukan Zamfara.

Jami’an rundunar sojin saman Najeriya sun yi ruwan bama-bamai a sansanonin ‘yan bindigar da ke tsakanin al’umomin Zurmi da Birnin Magaji a jihar Zamfara da Jibia a jihar Katsina, kamar yadda wata majiyar tsaro ta bayyana.

Kwanaki kadan kafin tashin bam din, an kai wani hari makamancin wannan a sansanin na wani sarkin ‘yan bindiga, Bello Turji da ke unguwar Fakai a jihar, inda aka kashe ‘yan bindiga a kalla 22, yayin da Turji ya tsere.

A cewar wata majiya daga yankin, Abdulbaqi Aliyu, harin na baya-bayan nan ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindiga a kalla 40 a yankin Birnin Magaji na jihar.

“Rundunar sojin saman Najeriya ta kai farmaki a dajin Sabon Birini Dan Ali, a karamar hukumar Birini Magaji, wanda ya yi sanadin kashe ‘yan fashin sama da 40,” inji shi.

An kai harin ne a lokacin da aka ce gungun na lodin shanun da aka sace.

“Ba a bayyana adadin mutanen da aka kashe a wannan farmakin ba saboda ‘yan bindigar sun taru a gidan Dan Karami domin yin taro. Babu tabbas ko yana cikin wadanda aka kashe,” inji majiyar.

Kawo yanzu dai babu wata sanarwa a hukumance daga Abdul Olaitan, kakakin rundunar sojin sama a jihar Katsina yayin da bai amsa kiran manema labarai ba.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...
X whatsapp