fidelitybank

Sojojin Sama sun kama mai garkuwa da mutane a Kano

Date:

Jami’an rundunar sojin saman Najeriya NAF, sun kama wani matashi dan shekara 35 da ake zargi da yin garkuwa da mutane mai suna Isah Abdul, wanda ake kyautata zaton yana da hannu wajen yin garkuwa da mutane da dama a bayan garin Kano.

A cewar NAF, an kama mutumin ne a ranar 19 ga watan Fabrairun 2024 da misalin karfe 6.30 na yamma a wani aiki na hadin gwiwa bayan samun bayanan sirri kan maboyar wanda ake zargin mai garkuwa da mutane ne da kungiyarsa.

Air Vice Marshal Edward Gabkwet, Daraktan Hulda da Jama’a da Yada Labarai na Rundunar Sojojin Saman Najeriya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

A cewarsa, an kama wanda ake zargin ne a Durbundai a karamar hukumar TakaiĀ  a jihar Kano.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa Isah Abdul da ā€˜yan kungiyarsa ne suka yi garkuwa da wani Yakubu Ibrahim Tagaho, wanda aka fi sani da ā€œSarkin Noman Gaya,ā€ a ranar 6 ga Afrilu, 2023, daga gidansa da ke kauyen Tagaho a karamar hukumar Takai.

Ya kara da cewa, bayan wata guda an sako wanda aka kashen bayan an biya kudin fansa naira miliyan 30.

ā€œA cikin watan Disambar 2023, wannan mai laifin ya sace ā€˜yan uwa mata 2 da wasu 3 a kauye daya sannan ya sake su bayan karbar makudan kudin fansa.

Sanarwar ta kara da cewa, “Haka kuma yana da alhakin wasu ayyukan garkuwa da mutane saboda yana da alaka mai karfi da wasu sannnan kungiyoyin masu garkuwa da mutane kamar kungiyar Danbul Fulaku da ke aiki a karamar hukumar Takai.”

Sanarwar ta bayyana cewa a halin yanzu wanda ake zargin yana hannun rundunar sojin saman Najeriya, yayin da ake ci gaba da bincike.

Sanarwar ta kara da cewa nan ba da jimawa ba za a mika shi ga hukumomin da suka dace domin ci gaba da shari’a.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miʙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin Ę“an Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaʙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

ʊan takarar shugaban ʙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ʙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alʙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Ę“an ʙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp