Jamiāan rundunar sojin saman Najeriya NAF, sun kama wani matashi dan shekara 35 da ake zargi da yin garkuwa da mutane mai suna Isah Abdul, wanda ake kyautata zaton yana da hannu wajen yin garkuwa da mutane da dama a bayan garin Kano.
A cewar NAF, an kama mutumin ne a ranar 19 ga watan Fabrairun 2024 da misalin karfe 6.30 na yamma a wani aiki na hadin gwiwa bayan samun bayanan sirri kan maboyar wanda ake zargin mai garkuwa da mutane ne da kungiyarsa.
Air Vice Marshal Edward Gabkwet, Daraktan Hulda da Jama’a da Yada Labarai na Rundunar Sojojin Saman Najeriya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.
A cewarsa, an kama wanda ake zargin ne a Durbundai a karamar hukumar TakaiĀ a jihar Kano.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa Isah Abdul da āyan kungiyarsa ne suka yi garkuwa da wani Yakubu Ibrahim Tagaho, wanda aka fi sani da āSarkin Noman Gaya,ā a ranar 6 ga Afrilu, 2023, daga gidansa da ke kauyen Tagaho a karamar hukumar Takai.
Ya kara da cewa, bayan wata guda an sako wanda aka kashen bayan an biya kudin fansa naira miliyan 30.
āA cikin watan Disambar 2023, wannan mai laifin ya sace āyan uwa mata 2 da wasu 3 a kauye daya sannan ya sake su bayan karbar makudan kudin fansa.
Sanarwar ta kara da cewa, “Haka kuma yana da alhakin wasu ayyukan garkuwa da mutane saboda yana da alaka mai karfi da wasu sannnan kungiyoyin masu garkuwa da mutane kamar kungiyar Danbul Fulaku da ke aiki a karamar hukumar Takai.”
Sanarwar ta bayyana cewa a halin yanzu wanda ake zargin yana hannun rundunar sojin saman Najeriya, yayin da ake ci gaba da bincike.
Sanarwar ta kara da cewa nan ba da jimawa ba za a mika shi ga hukumomin da suka dace domin ci gaba da shari’a.