Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya umurci sojojin Isra’ila da su ci gaba da luguden wuta da kan wuraren ‘yan ƙungiyar Hezbollah a Lebanon, duk da kiraye-kirayen tsagaita wuta da ake yi.
Wakiliyar BBC ta ce ofishin firaiministan Isra’ila ya fidda sanarwar da ta ce firaiminista bai ce komai ba game da buƙatar Amurka da Isra’ila.
Ministan harkokin wajen Isra’ila ya ce ba za a tsagaita wuta ba, har sai an samu nasara a kan Hezbollah.
Wani ministan Isra’ila mai ra’ayin riƙau Bezalel Smotrich ya yi watsi da shawarar tsagaita buɗe wuta, yayin da shugaban ƴan adawa Yair Lapid (Ya’ir Lipid) ya ce ya kamata a samu tsagaita wuta amma ta mako ɗaya kacal.