Ma’aikatar lafiya a Falasdinu ta ce, sojojin Isra’ila sun harbe wani matashi a wani samame da suka kai wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke gabar yammacin kogin Jordan.
Haka kuma sun ce wani matashi dan shekara sha takwas ya ji mummunan rauni.
Sansanin ‘yan gudun hijira na Jenin wuri ne da ake yawan samun rikici tsakanin sojojin Isra’ila da Falasdinawa.
A makon da ya gabata ne aka harbe wata yar jaridar Aljazeera Shireen Abu Akleh a wajen, lokacin da take ba da labarin wani hari da Isra’ila ta kai sansanin.