Rundunar sojan Nijar ta ce sauran sojojin Faransa 157 da ke ƙasar za su kammala janyewarsu nan da ranar 22 ga watan Disamba.
Dakarun da suka rage sun fito ne daga tawagogin da ke kula da kayan aiki daga farkon dakaru 1,346 da aka tura a yankin Sahel, in ji runudunar sojin a cikin wata sanarwa da ta fitar ta X.
An dai samu takun saka tsakanin Faransa da Nijar biyo bayan juyin mulkin ranar 26 ga watan Yuli ƙarƙashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani wanda ya hamɓarar da zabaɓɓen shugaban ƙasar, Mohamed Bazoum.
Bayan an ɗauki tsawon lokaci ana gwabzawa, Faransa ta fara janye sojojinta daga Nijar a cikin watan Oktoba, a daidai lokacin da gwamnatin mulkin sojan kasar ta buƙaci Faransawa da su fice, bisa zarginsu da yunkurin dawo da shugaba Bazoum da karfin tsiya.
Gwamnatin mulkin sojan ta kuma ce tana shirin kawo karshen wasu yarjejeniyoyin soja da na tattalin arziki da aka cimma da Paris.
Ana kallon Nijar a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen yammacin duniya a yankin Sahel da keyaƙi da ta’addanci.
Tasirin Faransa a Nijar na raguwa bayan juyin mulkin da aka yi a wasu ƙasashen da ta yi wa mulkin mallaka..