fidelitybank

Sojojin Faransa ku gaggauta ficewa daga kasar mu – Nijar

Date:

Rundunar sojan Nijar ta ce sauran sojojin Faransa 157 da ke ƙasar za su kammala janyewarsu nan da ranar 22 ga watan Disamba.

Dakarun da suka rage sun fito ne daga tawagogin da ke kula da kayan aiki daga farkon dakaru 1,346 da aka tura a yankin Sahel, in ji runudunar sojin a cikin wata sanarwa da ta fitar ta X.

An dai samu takun saka tsakanin Faransa da Nijar biyo bayan juyin mulkin ranar 26 ga watan Yuli ƙarƙashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani wanda ya hamɓarar da zabaɓɓen shugaban ƙasar, Mohamed Bazoum.

Bayan an ɗauki tsawon lokaci ana gwabzawa, Faransa ta fara janye sojojinta daga Nijar a cikin watan Oktoba, a daidai lokacin da gwamnatin mulkin sojan kasar ta buƙaci Faransawa da su fice, bisa zarginsu da yunkurin dawo da shugaba Bazoum da karfin tsiya.

Gwamnatin mulkin sojan ta kuma ce tana shirin kawo karshen wasu yarjejeniyoyin soja da na tattalin arziki da aka cimma da Paris.

Ana kallon Nijar a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen yammacin duniya a yankin Sahel da keyaƙi da ta’addanci.

Tasirin Faransa a Nijar na raguwa bayan juyin mulkin da aka yi a wasu ƙasashen da ta yi wa mulkin mallaka..

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp