fidelitybank

Sojojin da suka yi juyin mulki sun saki shugaban da suka tuntsurar

Date:

Sojojin da suka yi juyin mulki a Gabon sun bayyana kawo ƙarshen ɗaurin talalar da suke yi wa hamɓararren shugaban ƙasar Ali Bongo, suna masu cewa a yanzu yana da damar barin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin mulkin sojin, Kanal Ulrich Manfoumbi, sojojin suka karanta a gidan talbijin na ƙasar ranar Laraba da maraice, ya ce an saki Ali Bongo ne bisa dalilai na rashin lafiya.

“A yanzu, idan ya ga dama yana iya fita daga ƙasar domin a duba lafiyarsa,” in ji sanarwar.

Tun bayan da sojojin suka kifar da gwamnatin Ali Bongo ranar 30 ga watan Agusta ne suka ci gaba da tsare a gidansa.

Matakin sakin hamɓararren shugaban ƙasar na zuwa ne bayan da sojojin suke ta samun matsin lamba daga ƙungiyar ƙasashen tsakiyar Afirka da ECCAS da kuma maƙwabtan ƙasar na cewa su martaba lafiya tare da mutunta hamɓararren shugaban ƙasar

A shekarar 2018 ne dai, Ali Bongo ya gamu da cutar shanyewar ɓarin jiki.

Yanayin lafiyarsa ya kasance abin damuwa musamman a lokacin yaƙin neman zaɓe.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp