fidelitybank

Sojoji za su gudanar da bincike a kan kisan malamin addinin Yobe

Date:

Rundunar sojoji ta ce, ta kaddamar da bincike kan kisan da aka yi wa fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na jihar Yobe, Sheikh Goni Aisami.

Mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar ta biyu ta Operation Hadin Kai, Kennedy Anyawu, ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi a Damaturu. In ji BBC.

Rundunar ta ce tuni ta kama sojoji biyu, kofur John Gabriel da kofur Adamu Gideon a kan batun kisan malamin.

Rundunar da hadin gwiwar rundunar ‘yan sandan jihar Yobe ne za su gudanar da bincike don gano wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Kazalika rundunar ta kuma kafa wani kwamiti da zai bankado yadda lamarin ya auku.

Idan aka kammala bincike aka gano wadanda suka aikata kisan to lallai za su fuskanci hukunci da ya kamata in ji rundunar.

Kisan malamin É—an Jihar Yobe ya ja hankalin ‘yan Æ™asar musamman ma’abota shafukan zumunta.

A ranar Juma’ar da ta wuce ne aka kashe malamin a lokacin da yake tuÆ™a motarsa a kan hanyar zuwa Gashua daga Nguru.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp