Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Asabar din da ta gabata ta kai farmaki maboyar ‘yan ta’adda a kauyen Tandama da ke karamar hukumar Danja tare da ceto wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su.
Sanarwar da Kakakin Rundunar, Sufeto Gambo Isah ya fitar, ya ce, an kai samame maboyar ‘yan ta’addar ne bisa sahihan bayanan sirri.
Ya ce: “A ranar Asabar 6/08/2022 da misalin karfe 0530 na safe, bisa samun sahihan bayanan sirri, rundunar ‘yan sandan ta kai farmaki maboyar ‘yan ta’adda a Unguwan Dako, kauyen Tandama, a karamar hukumar Danja, inda ta yi nasarar ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su.
”Su ne: Alhaji Garba Dan Mallam, M,52 of Unguwan Nuhu, Danja LGA ,Rabiu Idris,45 of the same address, Abba Samaila, 38, Yunusa Sani, 54 of Layin Sani village, Kafur Ishaq Yakub, 40,Danjuma Samaila, mai shekaru 45, duk adireshin daya ne.”
A wani labarin kuma, wani rahoto da ba a tabbatar da shi ba daga wasu al’ummar garin Safana ya nunar da harin bam din da rundunar sojojin saman Najeriya NAF ta kai a wani sansanin ‘yan ta’adda da ke karamar hukumar Safana ta jihar Katsina a yammacin ranar Asabar da ta kai ga halaka shugaban ‘yan ta’adda Abdulkarim Faca- faca.
Hakazalika an kashe wasu gungun ‘yan ta’adda takwas da ake zargin ‘yan ta’adda ne a yayin farmakin NAF, yayin da wasu ‘yan ta’addan suka tsere da raunukan harbin bindiga a lokacin da ake gudanar da aikin share fage.