fidelitybank

Sojoji sun yi lugudan ruwan wuta a Borno da Zamfara

Date:

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce, ta kashe ƴan bindiga masu yawa a yayin wasu hare-hare ta sama da ta ƙaddamar kan maɓoyar ‘yan ta’adda a wasu sassan ƙasar nan.

Cikin wata sanarwar da rundunar ta fitar ranar Lahadi, mai ɗauke da sa hannun daraktan hulɗa da jama’a na rundunar, Air Commodore Edward Gabkwet, ta ce dakarun sojin ƙarƙashin haɗin gwiwar rundunonin Hadin Kai da ta Hadarin Daji sun kai hare-hare kan ‘yan ta’adda a Bukar Meram, kusa da Tafkin Chadi a jihar Borno da kuma yankin Sangeko a jihar Zamfara.

Air Commodore Edward Gabkwet, ya ce rundunar ta ƙaddamar da hare-haren ne bayan da ta samu bayanai game da sauya matsuguni da ‘yan bindigar ke yi.

Harin farko an kai shi a lokacin da ‘yan bindigar ke ƙaura daga Suwa zuwa yankin Bukar Meram, domin shirya kai hare-hare kan fararen hula da sojoji, kamar yadda sanarawar ta bayyana.

Sanarwar ta ƙara da cewa harin ya samu nasarar halaka ‘yan ta’addan masu yawan gaske tare da lalata babura fiye da 40 da motocin da ke dakon makamai ga ‘yan bindigar.

Haka kuma Gabkwet ya ce sojojin ƙarƙashin rundunar Hadarin Daji, sun ƙaddamar da makamancin irin wannan hari ranar 11 ga watan Oktaba a yankin Sangeko da ke ƙaramar hukumar Maru a jihar Zamfara.

Ya ƙara da cewa dakarun sun kai hari kan ‘yan ta’addan waɗanda ke tafiya cikin jerin gwanon babura kimanin 70 a kan hanya daga Kabaro zuwa Sangeko, inda aka kashe da dama da jikkata wasu,tare da lalata babura masu yawa.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp