Rundunar sojan Najeriya ta tabbatar da tarwatsa sansanin ƙungiyar Boko Haram a Jihar Borno da ke Gabashin ƙasar nan.
Wani saƙo da ta wallafa a shafukanta na sada zumunta sun nuna yadda aka tarwatsa motar mayaƙan da ake kai harin bam da ita da ake yi wa laƙabi da Vehicle Borne Improvised Explosive Device (VBIED).
Sanarwar ta ƙara da cewa, dakarun rundunar Operation Desert Sanity ne suka kai harin a jiya Laraba a yankin Njimia-Alafa.
A cewar rundunar, har yanzu suna ci gaba da aikin zaƙulo ‘yan ƙungiyar a dazukan da suke ɓoye. In ji BBC.