Dakarun soji na rundunar Hadin kai, da ke yaki da Boko Haram a Najeriya, sun tabbatar da sake gano wata ‘yar makarantar Chibok mai suna Ruth Bitrus, wacce ta kubuta daga hannun mayakan Boko Haram tare da danta.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, babban kwamandan dakarun rundunar, Manjor janar GC Musa na bayyana hakan ranar Laraba.
A lokacin da yake mika wasu magunguna da hukumar raya yankin arewa maso gabas ta bai wa sojojin da ke aiki a yankin.
Kwamandan ya ce ”Idan za ku iya tunawa makonni da suka gabata, mun kubutar da ‘yan matan Chibok biyu, to yanzu ma mun sake kubutar da wata guda daya”
A ‘yan kwanakin baya ne dai, dakarun suka kubutar da ‘yan mata biyu a karamar hukumar Gazuwa.