fidelitybank

Sojoji sun ragargaji Ƴan Ta’adda 21 a Katsina

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta hallaka wasu ƴan bindiga 21 a dajin Shawu a karamar hukumar Faskari na jihar Katsina.

Wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafinta na X, ta ce dakarunta na Operation Fansan Yamma ne suka samu nasarar kashe ƴan bindigar bayan kai musu hari a maɓoyarsu ranar 23 ga watan Mayu, a ci gaba da yaƙi ayyukan ɓata-garin.

Sanarwar ta ce an samu nasarar kashe ƴan bindigar ne bayan artabu na tsawon lokaci, ciki har da waɗanda kogi ya tafi da su lokacin da suke ƙoƙarin tserewa.

Sai dai sanarwar ba ta bayar da rahoton mutuwar wani jami’in soji ba a artabun da aka yi.

Ta kuma ce an ƙwato mamakai da harsasai da dama – ciki har da babura 40 da shanu da dama waɗanda ƴan bindigar suka sace.

Har ila yau, sojojin sun ce samamen da suka kai ya sa ƴan bindigar tserewa tare da barin sansaninsu, inda suka fantsama cikin dazuka.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...
X whatsapp