Rundunar Sojin Saman Najeriya ta tabbatar da kashe ƴan bindiga da dama a Parisu, kusa da dajin Sambisa sakamakon hare-haren da ta kai, ta kuma kai makamancin harin a Tumbun Agiri da ke Tafkin Chadi.
Rundunar sojin saman cikin wata sanarwa da ta fitar jiya Lahadi ta ce ta samu nasara sakamakon haɗin gwiwa daga sojojin da ke aiki ƙarƙashin rundunar Hadin Kai da ke jihar Borno, a yankin arewa maso gabashin Najeriya.
Kakakin rundunar sojin saman, Edward Gabkwet ya ce a ranar 5 ga watan Janairu ne aka kai samamen na Parisu yayin washe garin ranar kuma, sojoji suka far wa ƴan bindigar da ke Tafkin Chadi.
A cewar rundunar, an kashe ƴan bindiga 12 a Parisu sannan an lalata kayayyakin aikinsu lamarin da ya rage musu ƙarfi wajen kai hari ko haɗa runduna ta kansu.
Dangane da samamen da aka kai a Tafkin Chad kuma, rundunar ta ce hare-haren da aka akai sun lalata motoci da baburan ƴan bindigar tare da kashe wasu daga cikinsu da dama.