fidelitybank

Sojoji sun ragargaji mayaƙan Boko Haram 48

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta yi nasarar kashe mayaƙan Boko Haram 48, sannan wasu 974 sun ajiye makamai tare da miƙa wuya.

Daraktan yaɗa labaran hedkwatar tsaron ƙasar, Manjo Janar Musa Danmadami ya bayyana wa manema labarai cewa ƴan ta-da-ƙayar-bayan sun miƙa wuya ne haɗe da iyalansu cikin makonni biyu da suka gabata.

Ya ce rundunar ta yi amfani da salo iri daban-daban wajen kai hare-hare “a kan ƴan ta’addan Boko Haram”.

Danmadami ya ce dakarunsu na Operation Haɗin Kai sun ƙaddamar da wasu hare-hare a kan ƴan Boko Haram ranar 23 ga watan Maris, cikin ƙananan hukumomin Askira Uba da Mafa da kuma Bama, inda suka kashe bakwai daga cikinsu yayin da wasu kuma suka tsere.

Ya ce sun yi nasarar ƙwato kayayyaki da makamai masu yawa kama daga kayan haɗa bama-bamai da kekuna da babura da sauransu.

Karanta Wannan: Faɗan ƙabilanci ya yi sanadiyar mutuwar mutane a Taraba

Danmadami ya ce sun kuma samu nasarar tarwatsa maɓoyar ƴan ta-da-ƙayar-bayan abin da ya yi sanadin mutuwar da dama a cikinsu da jikkata wasu.

Ya ce hare-haren da suka ƙaddamar da jiragen sama kuma, sun lalata kayayyakin ƴan Boko Haram.

A baya-bayan nan, dubban mayaƙan Boko Haram ne suka miƙa wuya ga sojojin Najeriya, mai yiwuwa saboda matsin lambar da suke fuskanta daga dakarun ƙasar.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi...

Ba mu yarda da zaben Ghari da Tsanyawa ba – NNPP

Jam'iyar NNPP mai mulkin jihar Kano a arewacin Najeriya...

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...
X whatsapp