fidelitybank

Sojoji sun ragargaji mayaƙan Boko Haram 48

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta yi nasarar kashe mayaƙan Boko Haram 48, sannan wasu 974 sun ajiye makamai tare da miƙa wuya.

Daraktan yaɗa labaran hedkwatar tsaron ƙasar, Manjo Janar Musa Danmadami ya bayyana wa manema labarai cewa ƴan ta-da-ƙayar-bayan sun miƙa wuya ne haɗe da iyalansu cikin makonni biyu da suka gabata.

Ya ce rundunar ta yi amfani da salo iri daban-daban wajen kai hare-hare “a kan ƴan ta’addan Boko Haram”.

Danmadami ya ce dakarunsu na Operation Haɗin Kai sun ƙaddamar da wasu hare-hare a kan ƴan Boko Haram ranar 23 ga watan Maris, cikin ƙananan hukumomin Askira Uba da Mafa da kuma Bama, inda suka kashe bakwai daga cikinsu yayin da wasu kuma suka tsere.

Ya ce sun yi nasarar ƙwato kayayyaki da makamai masu yawa kama daga kayan haɗa bama-bamai da kekuna da babura da sauransu.

Karanta Wannan: Faɗan ƙabilanci ya yi sanadiyar mutuwar mutane a Taraba

Danmadami ya ce sun kuma samu nasarar tarwatsa maɓoyar ƴan ta-da-ƙayar-bayan abin da ya yi sanadin mutuwar da dama a cikinsu da jikkata wasu.

Ya ce hare-haren da suka ƙaddamar da jiragen sama kuma, sun lalata kayayyakin ƴan Boko Haram.

A baya-bayan nan, dubban mayaƙan Boko Haram ne suka miƙa wuya ga sojojin Najeriya, mai yiwuwa saboda matsin lambar da suke fuskanta daga dakarun ƙasar.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp