fidelitybank

Sojoji sun ragargaji ƴan Boko Haram 52

Date:

Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce dakarunta sun yi nasarar kashe ƴan ta’adda 52 da kama 53 a wasu samame da suka kai jihohin Borno da Yobe.

Mai magana da yawun hedkwatar sojojin, Manjo-Janar Edward Buba, shi ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Juma’a, inda ya ce ƴan ta’adda bakwai da suka haɗa maza biyar da mata biyu sun miƙa kansu ga sojojin.

Janar Buba ya ce an kuɓuto da mutum 61 da aka yi garkuwa da su a wurare daban-daban da ke ƙasar.

Ya kuma ce dakarun Operation Haɗin Kai a yankin arewa maso gabas, sun yi artabu da ƴan ta’addan a lokacin da suka kai samame, inda suka samu nasarar ƙwato makamai da dama.

A ɗayan ɓangare, ya ce dakarun Operation Delta Safe sun samu nasarar kama masu satar ɗanyen man fetur, inda suka kwace lita 496, 250 na ɗanyen mai, injunan tuka-tuka guda huɗu, jiragen ruwa biyar da tankunan ajiye mai 57 da sauransu.

Janar Edward ya ce baya ga wannan, sojojin sun kwace harsasai daban-daban daga wajen masu aikata ta’asar.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp