fidelitybank

Sojoji sun nemi afuwar ƴan Kaduna

Date:

Babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya, Janar Taoreed Lagbaja, ya nemi afuwa daga al’ummar ƙauyen Tudun Biri da ke jihar Kaduna, kan wani harin jirgin maras matuƙi da ya kashe mutane a ranar Lahadi.

A wata sanarwa da rundunar sojin ƙasa ta Najeriyar ta wallafa a shafinta na sada zumunta, ta bayyana cewa babban hafsan sojin ƙasan na Najeriya ya kai ziyarar jaje a ƙauyen yau Talata inda “ya nuna nadama game da mummunan lamarin.”

Janar Lagbaja ya ce lamarin ya faru ne yayin da dakarun sama na ƙasar ke gudanar da wani sintiri ta sama, inda suka tsinkayi gungun mutane “waɗanda suka yi kuskuren fassara abubuwan da suke yi” a matsayin tamkar irin na ƴan fashi, wanda hakan ya sa aka kai musu hari.

Ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike domin “gano inda aka samu naƙasun da ya haifar da wannan mummunan abu,” inda za a yi amfani da sakamakon binciken domin daƙile faruwar irin hakan a gaba.

Al’ummar Najeriya da dama sun nuna fusata kan lamarin, wanda shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya bayar da umarnin gudanar da bincike a kai.

Tuni dai hukumar agajin gaggawa ta ƙasa ta bayyana cewa mutum 85 ne suka rasu sanadiyyar harin, yayin da wasu mutanen 60 suka samu rauni, sai dai ƙungiyoyin masu kare hakkin bil’adama na ganin cewa alƙaluman sun zarce haka.

An dai samu irin wannan kuskure a baya, inda hare-haren na sojojin Najeriya ke shafar fararen hula.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp