fidelitybank

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Date:

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar da gagarumin farmakin sama kan sansanonin ‘yan bindiga a jihar Neja a ranakun Laraba da Alhamis, a wani yunƙuri na kawar da ƴan fashin da suka kai hari kan dakarun ƙasar a baya-bayan nan.

Wata sanarwa da rundunar sojin saman ta wallafa a shafinta na sada zumunta ta ce an kai harin ne ƙarƙashin shirin FANSAN YAMMA “domin kawar da barazanar tsaro da ‘yan ta’adda ke haifarwa.

“A ranar 26 ga watan Yuni, bayan samun bayanan sirri, rundunar sojin saman Najeriya, bayan haɗa gwiwa da sauran jami’an tsaro ta gano ayyukan ƴan bindiga da suka hada da satar shanu a yankin Kakihun da Kumbashi,” in ji sanarwar wadda ta samu sa hannu daraktan yaɗa labarai na rundunar Air Commodore Ehimen Ejodame.

“Nan take rundunar ta ƙaddamar da hare-haren da suka yi sanadin kashe ƴan fashin daji da dama, lalata kayan aikinsu da kuma hana su haɗuwa,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

A cikin makon nan ne aka samu rahotannin da suka ce ƴan fashin daji a jihar ta Neja, arewa maso tsakiyar Najeriya sun kai samame a wasu sansanonin sojin Najeriya inda suka kashe jami’an soji “aƙalla 17”.

Wata sanarwa da rundunar sojin ƙasa ta Najeriyar ta fitar ta tabbatar da kai harin sai dai ba ta yi bayani kan yawan sojojin da suka rasa rayukansu ba sanadiyyar farmakin.

Neja na cikin jihohin Najeriya masu fama da matsalar tsaro, inda ƴan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka da dama, lamarin da ya haifar da asarar ɗimbin rayuka da kawo cikas ga ayyukan tattalin arziƙi.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...
X whatsapp