fidelitybank

Sojoji sun lalata wak3n ƙera abubuwan fashewa a Borno

Date:

Rundunar sojin saman ƙasar nan ta ce, ta lalata wani sansani da take zargin mayaƙan Boko Haram na ƙera abubuwan fashewa a tsaunukan Mandara da ke jihar Borno.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce, sakamakon yadda a baya-bayan nan mayaƙan Boko Haram ke amfani da abubuwan fashewa wajen kashe fararen hular da ba su ji ba su gani ba, musamman a jihar Borno, ya sa jami’anta suka tsananta bincike domin gano inda mayaƙan ƙungiyar ke ƙera abubuwan fashewar.

..Asalin hoton,NAF/X
Sanarwar ta ce wasu bayanan sirri da sojojin suka samu sun bayyana mata cewa akwai wata masana’anta da ake ƙera abubuwan fashewar da kuma adana su a tsaunin Mandara.

Sojojin saman na Najeriya sun ce bayanan sun tabbatar mata cewa an sauya wa masana’antar matsuguni daga Gwoza zuwa Timbuktu a dajin Sambisa kafin dagabisani a mayar da shi yankin Grazah da ke tsaunin Mandara.

”Sakamakon tsananta hare-hare kan mayaƙan da sojoji ke yi a baya-bayan nan ya sa aka mayar da ɗauke masana’antar daga dajin Sambisa zuwa tsaunukan na Mandara”, in ji sanarwar sojojin.

sojojiAsalin hoton,NAF/X
Sojojin sun ce sun shafe tsawon makonni suna sanya ido kan wurin ƙera abubuwan fashewar da sauran ayyukan mayaƙan a yankin.

”A lokacin da muka ƙaddamar da harin, mun hangi wasu manyan motocin dakon makamai guda biyu a kusa da masana’antar, tsaye ƙarƙashin bishiya”, in ji sanarwar.

”Hakan ne ya sa ba mu yi wata-wata ba muka ƙaddamar da hare-hare a yankin, da nufin lalata masana’antar tare da kashe mayaƙan ƙungiyar”.

Sanarwar ta ci gaba da cewa sojojin sun samu nasarar lalata masana’antar.

Hotunan bayan harin sun nuna yadda wurin ya turnuƙe ta hayaƙi, bayan da masana’antar ta ƙone tare da motocin dakon makaman guda biyu

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp