fidelitybank

Sojoji sun lalata haramtattun wuraren tace mai a Najeriya

Date:

Dakarun sojan Najeriya sun lalata haramtattun wuraren tace man fetur 30, sannan suka kwashe sama da lita miliyan 12 na gas da ababen hawa ke amfani da shi (AGO) a ayyukan da suka yi a jihohin Delta, da Rivers, da Bayelsa.

Daraktan yada labarai na rundunar sojan, Manjo Janar Bernard Onyeuko, shi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai ranar Alhamis a Abuja.

Kamar yadda sanarwar tace, “Sojojin sun gano tare da lalata haramtattun wuraren tace mai 30, da tankunan ajiye 37, da tanda 31, da manyan jiragen ruwa na katako 12, da na’urorin sanyaya wuri biyu, da ramukan ajiya uku, da ganguna na Æ™arfe,” a cewarsa.

“A dunkule, sojojin sun kwato litar mai miliyan 12, da tataccen litar gas 150,000, da lita 4,000 na danyen mai da aka sata, da motocin tanka uku, da motoci uku, da bututu 73, da babura biyu, da motar bas daya, da Toyota kirar Camry daya, da ƙirar Mercedes Benz daya.

“Bugu da kari, an kama wasu barayin manyan wayoyin wutar lantarki biyu da ke da alaka da lalatawa da kuma sata.”

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuÉ—in...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp