fidelitybank

Sojoji sun kuɓutar da mutane 20 a jihar Katsina

Date:

Rundunar sojan kasar nan ta ce dakarunta sun ceto wasu mata kusan 20 daga masu garkuwa da mutane a jihar Katsina tare da mika su hannun hukumomin jihar.

Sojojin sun ce sun samu nasarar kubutar da mutanen ne yayin wasu hare-haren da suka kai kan maboyar ‘yan bindigar a dazukan ‘yan-tumaki da Dan-Ali.

Hakan dai na zuwa ne bayan sace wasu mata 53 da ke kan hanyarsu ta zuwa kai amarya a yankin karamar hukumar Sabuwa.

A lokacin da ya yi wa BBC ƙarin bayani, kwamishinan harkokin tsaro na jihar Katsina, Nasir Mu’azu ya ce babu tabbas kan lokacin da aka sace mutanen da aka ceton.

Sai dai ya bayyana cewa mutanen da aka ceton ƴan asalin ƙaramar hukumar Musawa ne da ke jihar.

Ko a makon da ya gabata, wasu ƴan bindiga sun sace ƴan rakiyar amarya sama da 50 a ƙaramar hukumar Sabuwa, waɗanda masu garkuwa da mutanen suka yi barazanar sayar da su da kuma sake aurar da amaryar.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp