Rundunar sojin ruwa ta kuɓutar da mutum 18 da aka yi safarsu a unguwar Rijiyar Lemu da ke ƙaramar hukumar Ungogo a jihar Kano da ke arewacin Najeriya
A wani saƙo da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce ta kama mutum biyu da take zargi da hannu wajen safarar mutanen.
Karanta Wannan: Ganduje ya dakatar da Buhari zuwa Kano
Rundunar ta ce, ta samu nasarar kuɓutar da mutanen ne bayan da wani jami’insu ya ankarar da su kasancewa ‘yar uwarsa na daga cikin mutanen da aka yi safar ta su.
Sojojin ruwan sun ce, sun miƙa mutanen tare da waɗanda ake zargin hannun hukumar da ke yaƙi da safarar bil-adama ta ƙasar domin ɗaukar mataki.