fidelitybank

Sojoji sun kuɓutar da Mutanen da aka yi garkuwa da su a Taraba

Date:

Bayan samun rahoton gaggawa kan ayyukan ‘yan bindiga a wannan yankin a ranar 13 ga Disamba, 2024, sojojin sun dauki mataki nan take inda suka isa wurin. Bayan fafatawa da masu garkuwa, sun samu nasarar kubutar da mutane uku.

A cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojoji ta 6, Olubodunde Oni, ya ce wadanda aka kubutar din sun koma ga iyalansu lafiya.

Daga nan, sojojin sun gudanar da sintirin yaki a yankunan tsaunuka tare da gano wuraren da ake samun barazana a kananan hukumomin Ardo-Kola da Yorro, domin kara tabbatar da tsaro da doka.

Haka kuma, a ranar 12 ga Disamba, 2024, yayin da sojojin ke sintiri a kan titin Takum zuwa Katsina Ala, sun tarar da wani harin fashi da akeyi a kusa da Kasuwan Shanu da ke garin Takum.

Dabarun gaggawa sun kai ga cafke wani da ake zargi da fashi da makami mai suna Emmanuel Thomas Oryiman, wanda aka samu da bindiga da aka kera a gida da harsasai biyu na 9mm.

Kwamandan Runduna ta 6 ta Sojojin Najeriya, Birgediya Janar Kingsley Uwa, ya bayyana cewa nasarorin da aka samu karkashin Aikin GOLDEN PEACE sun yi nufin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Taraba da wasu sassan Jihar Benue.

Wannan mataki yana nufin hana ‘yan ta’adda damar aikata laifi tare da karfafa tsaro a cikin yankin da rundunar ke kula da shi.

Kwamandan ya yabawa jarumtaka da kwarewa, da saurin daukar matakin da sojojin suka nuna, sannan ya tabbatarwa da al’umma cewa Sojojin Najeriya za su ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyi.

Haka kuma, ya bukaci mazauna yankin su ci gaba da baiwa sojoji goyon baya ta hanyar bayar da sahihin bayani domin taimakawa wajen yaki da miyagun mutane.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp