fidelitybank

Sojoji sun kuɓutar da Mutanen da aka yi garkuwa da su a Taraba

Date:

Bayan samun rahoton gaggawa kan ayyukan ‘yan bindiga a wannan yankin a ranar 13 ga Disamba, 2024, sojojin sun dauki mataki nan take inda suka isa wurin. Bayan fafatawa da masu garkuwa, sun samu nasarar kubutar da mutane uku.

A cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojoji ta 6, Olubodunde Oni, ya ce wadanda aka kubutar din sun koma ga iyalansu lafiya.

Daga nan, sojojin sun gudanar da sintirin yaki a yankunan tsaunuka tare da gano wuraren da ake samun barazana a kananan hukumomin Ardo-Kola da Yorro, domin kara tabbatar da tsaro da doka.

Haka kuma, a ranar 12 ga Disamba, 2024, yayin da sojojin ke sintiri a kan titin Takum zuwa Katsina Ala, sun tarar da wani harin fashi da akeyi a kusa da Kasuwan Shanu da ke garin Takum.

Dabarun gaggawa sun kai ga cafke wani da ake zargi da fashi da makami mai suna Emmanuel Thomas Oryiman, wanda aka samu da bindiga da aka kera a gida da harsasai biyu na 9mm.

Kwamandan Runduna ta 6 ta Sojojin Najeriya, Birgediya Janar Kingsley Uwa, ya bayyana cewa nasarorin da aka samu karkashin Aikin GOLDEN PEACE sun yi nufin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Taraba da wasu sassan Jihar Benue.

Wannan mataki yana nufin hana ‘yan ta’adda damar aikata laifi tare da karfafa tsaro a cikin yankin da rundunar ke kula da shi.

Kwamandan ya yabawa jarumtaka da kwarewa, da saurin daukar matakin da sojojin suka nuna, sannan ya tabbatarwa da al’umma cewa Sojojin Najeriya za su ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyi.

Haka kuma, ya bukaci mazauna yankin su ci gaba da baiwa sojoji goyon baya ta hanyar bayar da sahihin bayani domin taimakawa wajen yaki da miyagun mutane.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp