Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta kubutar da wasu mutane 18 da aka sace tare da kwato wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba, bayan da suka yi artabu da ‘yan bindiga da suka kaddamar da hare-hare a jihar.
‘Yan ta’addan sun auka wa matafiya da ke kan hanyar Gusau da ke jihar Zamfara zuwa Funtuwa a jihar Katsina da wasu kauyuka da suka hada da kauyen Gidan Gada da ke karamar hukumar Kafur. A harin kwanton baunar da aka kai kan babbar hanyar, wasu mutane dauke da bindigogi kirar AK-47 sun tare motoci hudu da suka hada da manyan motocin DAF guda biyu, da Canter daya, da Toyota Avensis daya, suka kuma yi awon gaba da fasinjojin da ke cikin motar.
A halin da ake ciki sauran ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen Gidan Gada inda aka ce sun yi awon gaba da shanu tare da lalata kauyen.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, Abubakar Aliyu, yayin da yake tabbatar da afkuwar lamarin a cikin wata sanarwa, ya ce: “Nan take DPO na Kafur da Malumfashi sun hada rundunarsu tare da kai farmaki.”
Jami’an sun bi sawun ‘yan bindigar zuwa kauyen Fanisau, inda a sakamakon haka suka yi ta fafatawa da su, inda ‘yan bindigar suka gudu suka bar dabbobin da aka ceto da kuma wadanda aka kwato.
Sai dai DPO Kafur ya yi rashin sa’a domin ya samu raunin harbin bindiga; tun daga lokacin yana samun ingantaccen kulawar lafiya.
Aliyu ya ce, “Sau da gaggawar da DPO na Kafur da Malumfashi suka yi ne ya sa aka samu nasarar aikin, inda aka fatattaki ‘yan bindigar, kuma an kwato dabbobin da suka sace. Ana ci gaba da bin diddigin masu laifin da suka gudu domin a kama su.”
Daga nan sai Aliyu ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da taimaka wa jami’an tsaro wajen sauke nauyin da aka rataya a wuyansu da bayanai masu ma’ana kan ayyuka da motsin masu aikata laifuka.