fidelitybank

Sojoji sun kuɓutar da Ɗaliban Gusau

Date:

Sojojin Najeriya ƙarƙashin rundunar Hadarin Daji mai yaƙi da ‘yan fashin daji a arewacin Najeriya ta ce ta samu nasarar kuɓutar da wasu ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara, da ‘yan bindiga suka sace da da tsakar daren ranar Asabar 14 ga watan Octoba.

‘Yan bindigar sun far wa ɗaukanan kwanan ɗaliban da ke unguwar Sabon Gida, da ke yankin Damba a karamar hukumar Gusau, cikin dare a lokacin da daliban suka fara bacci.

Inda suka fara harbin kan mai tsautsayi, lamarin da ya sa suka yi garkuwa da ɗaliban.

Cikin wata sanarwar da Rundunar hadarin Daji ta fitar – mai ɗauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar, Kaftin Ibrahim Yahaya – ta ce rundunar ta samu nasarar kuɓutar da ɗaliban ne bayan da suka mayar da martani a kan lokaci yayin da aka sanar da su halin da ake ciki game da satar ɗaliban.

Sanarwar ta ce nan take rundunar haɗa kan dakarunta, inda suka datse hanyar da suke tunanin ‘yan bindigar za su ɓullo, inda suka yi musayar wuta da ‘yan bindigar.

“Matsin da ‘yan bindigar suka sha ya tilasta musu tserewa tare da barin ɗaliban”, in ji sanarwar.

A lokacin musayar wutar- wadda aka yi da misalin ƙarfe12 na dare, dalibai biyu sun samu guduwa da kansu, yayin da jami’an tsaro suka ceto biyu.

A baya- bayan nan ‘yan bindiga sun ɓullo da salon kai wa ɗaliban jami’o’i hari tare da sace su a ɗakunan kwanansu.

Ko a watan Satumba ma sai da ‘yan bindigar suka kai wa ɗaliban na FUGUS hari a ɗakunan kwanansu inda suka sace ɗalibai masu yawa, wani lamari da ya tayar da ƙura a ƙasar.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp