fidelitybank

Sojoji sun kashe ɗan fashin dajin Bauchi

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe dan fashi guda a wani ƙwanton-ɓauna da sojojin suka yi wa tawagar ‘yan fashin a yankin Bura na ƙaramar hukumar Ningi da ke jihar Bauchi.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Asabar, mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Burgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya ce sojojin sun amfani da bayanan sirri da suka samu game da ‘yan fashin.

“Sojojin sun yi wa ‘yan fashin kwanton-ɓauna tare da buɗe musu wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwar guda daga cikinsu, yayin da sauran suka tsere da raunukan harbin bingiga a jikinsu”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sojojin sun kuma ce sun samu nasarar ƙwato bindiga guda ƙirar Ak-47 da alburusai 14, da wayar hannu da kuma guru da layu daga ɗan fashin da suka kashe.

Sanarwar ta kuma ce sojojin na ci gaba da sintiri a yankin domin gano sauran ‘yan fashin da suka tsere.

Yankin arewa maso yammacin Najeriya ne dai ya fi fama da matsalar ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane, to sai dai a baya-bayan matsalar ta fara ɓulla a wasu yankunan jihar Bauchi da ke kudu maso gabashin ƙasar.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp