fidelitybank

Sojoji sun kashe ƴan fashin dajin Zamfara a ɓarin wuta

Date:

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Hadarin Daji daga arewa maso yamma, sun kashe ‘yan ta’adda hudu a jihar Zamfara.

An kashe su ne a lokacin da sojoji suka kai wa ‘yan fashin hari a wasu sansanoni da aka gano a kauyukan Tazame, Mashema, Gandaya, Maje, Doka da kuma yankunan da ke makwabtaka da kauyen Gandaya a karamar hukumar Bungudu ta jihar.

Sanarwar da hukumomin sojin suka fitar ta ce wasu ‘yan bindigar da ba a tabbatar da adadinsu ba sun tsere da yiwuwar harbin bindiga.

Sanarwar ta kuma tabbatar da cewa an kwato shanu hamsin da bakwai, da kakin soji, da kayan barci da kuma Naira dubu dari tara (tsabar kudi) daga maboyar ‘yan ta’addar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Dukkan ‘yan ta’addan da aka gano da kuma sansanonin wucin gadi an lalata su nan take a yayin farmakin”.

Wannan na zuwa ne sa’o’i ashirin da hudu bayan da sojojin suka kubutar da mutane 31 da aka yi garkuwa da su daga majiyar ‘yan bindiga a Sokoto, sannan kuma an lalata sansanoni da dama.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp