Sojoji sun kashe ƴan a-waren Biafra guda biyu da tarwasa sansanoninsu a jihar Imo.
Wata sanarwa da rundunar sojin Najeriyar ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce yayin samamen da dakarunta suka kai, sun kuma gano abubuwna fashewa da ƴan a-waren Biafran ke amfani da shi.
Sojojin sun ce sun dakarunsu sun ɗauki tsawon lokaci suna artabu tsakaninsu da ƴan ƙungiyar ta IPOB, kafin daga bisani su ci karfinsu tare da raunata da dama.
Sun kuma gano cewa ƴan IPOB ɗin na amfani da sansanonin wajen cin naman mutane da yin tsafi da kuma sanya tsoro a zukatan mutane.
Har ila yau, sanarwar ta ce an lalata gidajen wasu bokaye guda biyu tare da kama huɗu daga cikinsu.
Sojojin sun ce sun ƙwato wata tankar mai da babura huɗu da faifen zuko hasken lantarki da kuma kuɗaɗe.