fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda biyu a Kaduna

Date:

Rundunar sojin Najriya ta ce dakarunta da aka tura don daƙile ayyukan ƴan ta’adda a yankin arewa maso yamma sun yi wa wasu ‘yan bindiga kwantan-ɓauna, tare da kashe biyu daga cikinsu a jihar Kaduna.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojan Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, ta ce samamen da suka kai ranar Asabar, 13 ga watan Afrilu 2024, ya biyo bayan samun bayanai cewa an ga ‘yanbindigar suna safarar wani buhu mai dauke da makamai.

Sojojin sun kai samamen ne a kauyen Rafin Sariki da ke karamar hukumar Giwa na jihar.

“Dakarun mu sun yi artabu da ‘yan bindigar, kafin daga bisani su samu nasarar kashe biyu daga cikinsu,” in ji sanarwar.

Nwachukwu ya ce sun kuma kwato makamai da suka haɗa da bindigar AK-47 guda ɗaya, harsasai da kuma wani bindiga da aka kera cikin gida.

Sanarwar sojojin ta ce a shirye suke wajen tsaron rayuka da kuma dukiyoyin al’umma.

“Za mu ci gaba da ɗaukar matakai da suka dace kan ayyukan ƴan bindiga da suka addabi jama’ar yankin,” in ji sanarwar.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp