fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda biyu a Kaduna

Date:

Rundunar sojin Najriya ta ce dakarunta da aka tura don daƙile ayyukan ƴan ta’adda a yankin arewa maso yamma sun yi wa wasu ‘yan bindiga kwantan-ɓauna, tare da kashe biyu daga cikinsu a jihar Kaduna.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojan Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, ta ce samamen da suka kai ranar Asabar, 13 ga watan Afrilu 2024, ya biyo bayan samun bayanai cewa an ga ‘yanbindigar suna safarar wani buhu mai dauke da makamai.

Sojojin sun kai samamen ne a kauyen Rafin Sariki da ke karamar hukumar Giwa na jihar.

“Dakarun mu sun yi artabu da ‘yan bindigar, kafin daga bisani su samu nasarar kashe biyu daga cikinsu,” in ji sanarwar.

Nwachukwu ya ce sun kuma kwato makamai da suka haɗa da bindigar AK-47 guda ɗaya, harsasai da kuma wani bindiga da aka kera cikin gida.

Sanarwar sojojin ta ce a shirye suke wajen tsaron rayuka da kuma dukiyoyin al’umma.

“Za mu ci gaba da ɗaukar matakai da suka dace kan ayyukan ƴan bindiga da suka addabi jama’ar yankin,” in ji sanarwar.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp