fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan IPOB da suke nema ruwa a jallo

Date:

Rundunar soji ta kasa ta ce, ta kashe wasu ‘yan ƙungiyar IPOB biyu da take nema tare da lalata sansanin ƙungiyar a Jihar Imo da ke kudancin ƙasar.

Kakakin soji, Birgediya Janar Onyema Nwachuku, ya ce, dakarunsu tare da haɗin gwiwar ‘yan sandan DSS sun afka wa sansanin IPOB ranar Juma’a a Ƙaramar Hukumar Orlu.

“Dakaru sun lalata sansanin ba da horo bayan musayar wuta da su, inda aka kashe ƙasurguman miyagu biyu na ƙungiyar da ke cikin jerin mutanen da jami’an tsaro suka fi nema waɗanda suka addabi mazauna yankunan Orlu, da Orsu, da Njaba,” in ji sanarwar.

“Haka nan dakaru sun lalata wani wurin bauta da ‘yan ƙungiyar ke amfani da shi wajen yin addu’o’i, da kuma wani wurin haɗa makamai.”

Sanarwar ta ƙara da cewa, sojoji sun ƙwace bindigar harba-ruga uku da ƙaramar bindiga ƙirar gida da kuma layu da sauran makamai.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp