Rundunar soji ta kasa ta ce, ta kashe wasu ‘yan ƙungiyar IPOB biyu da take nema tare da lalata sansanin ƙungiyar a Jihar Imo da ke kudancin ƙasar.
Kakakin soji, Birgediya Janar Onyema Nwachuku, ya ce, dakarunsu tare da haɗin gwiwar ‘yan sandan DSS sun afka wa sansanin IPOB ranar Juma’a a Ƙaramar Hukumar Orlu.
“Dakaru sun lalata sansanin ba da horo bayan musayar wuta da su, inda aka kashe ƙasurguman miyagu biyu na ƙungiyar da ke cikin jerin mutanen da jami’an tsaro suka fi nema waɗanda suka addabi mazauna yankunan Orlu, da Orsu, da Njaba,” in ji sanarwar.
“Haka nan dakaru sun lalata wani wurin bauta da ‘yan ƙungiyar ke amfani da shi wajen yin addu’o’i, da kuma wani wurin haɗa makamai.”
Sanarwar ta ƙara da cewa, sojoji sun ƙwace bindigar harba-ruga uku da ƙaramar bindiga ƙirar gida da kuma layu da sauran makamai.
Rundunar soji ta kasa ta ce, ta kashe wasu ‘yan ƙungiyar IPOB biyu da take nema tare da lalata sansanin ƙungiyar a Jihar Imo da ke kudancin ƙasar.
Kakakin soji, Birgediya Janar Onyema Nwachuku, ya ce, dakarunsu tare da haɗin gwiwar ‘yan sandan DSS sun afka wa sansanin IPOB ranar Juma’a a Ƙaramar Hukumar Orlu.
“Dakaru sun lalata sansanin ba da horo bayan musayar wuta da su, inda aka kashe ƙasurguman miyagu biyu na ƙungiyar da ke cikin jerin mutanen da jami’an tsaro suka fi nema waɗanda suka addabi mazauna yankunan Orlu, da Orsu, da Njaba,” in ji sanarwar.
“Haka nan dakaru sun lalata wani wurin bauta da ‘yan ƙungiyar ke amfani da shi wajen yin addu’o’i, da kuma wani wurin haɗa makamai.”
Sanarwar ta ƙara da cewa, sojoji sun ƙwace bindigar harba-ruga uku da ƙaramar bindiga ƙirar gida da kuma layu da sauran makamai.