fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan Fashin Daji 10 a Zamfara

Date:

Dakarun sojin Najeriya, sun ceto wasu mutum tara da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Zamfara.

Kazalika, dakarun rundunar Hadarin Daji, sun kashe ‘yan fashin daji 10 a harin da ta kai a safiyar yau Talata.

Wata sanarwa daga rundunar ta ce dakaru sun samu bayanan sirri ne na ƴan bindigar da ke shirin sace wasu daga cikin waɗanda suka yi garkuwa da su daga jihar Sokoto zuwa ƙauyen Gadazaima na jihar Zamfara.

Sojojin sun yi kwanton-ɓauna a cikin ƙauyen, inda aka yi musayar wuta tsakanin sojojin da ƴan bindigar na tsawon sa’o’i.

“Ƴan bindiga 10 ne aka kashe, yayin da wasu da dama suka tsere bayan an jikkata su,” a cewar sanarwar.

“Da yawan ƴan bindigar sun nitse cikin wani kogi da ke kusa da ƙauyen a yayin da suke ƙoƙarin tserewa. An yi nasarar kama biyu da kuma makamai masu yawa, da ƙudi naira miliyan 2,410,000, da kuma keken ɗinki.”

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp