Akalla ‘yan ta’addar ISWAP da Boko Haram 21 ne suka mutu, sakamakon harin bam da sojoji suka kai musu a yankin tafkin Chadi da ke jihar Borno.
Wani rahoto da kafar yada labarai ta PRNigeria ta fitar ya bayyana cewa, an kawar da maharan ne a ranar Talata da wasu jirage masu saukar ungulu na yaki na rundunar sojojin saman Najeriya, NAF.
Wata majiyar leken asiri ta soji a yayin da take tabbatar da farmakin da jiragen NAF suka kai wa ‘yan ta’addan, ta lura da cewa, an kuma lalata maboyar ‘yan ta’addan a farmakin da suka kai na kwanan nan a Tumbun Jaki da Tumbun Murhu. In ji Daily Nigerian.
Ya ce: “Nasarar da aka samu ta kai hare-hare ta sama da aka gudanar a ranar 11 ga watan Yulin 2022 ya samo asali ne daga sahihan bayanan sirri kan ayyukan ‘yan ta’addan a wuraren da aka ambata da kuma mayar da martani ga hare-haren da aka kai a wuraren da sojoji suka yi a Damasak da Mallam Fatori.