fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Date:

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai a yankin arewa maso gabashin ƙsar sun halaka mayaƙan Boko Haram 17 yayin samamen da suka kai a sassan yankunan jihohin Borno da Adamawa.

Muƙaddashin Darakta a sashen hulɗa da jama’a na rundunar, Kyaptin Reuben Kovangiya, cikin wata sanarwa ya ce mayaƙan sun jima suna cin karensu babu babbaka a ƙananan hukumomin Bama da Konduga da Gwoza da Magumeri da Biu duka a jihar Borno da kuma Michika a jihar Adamawa.

Daily Trust ta ruwaito jami’in na cewa sojojin sun kuma gano tare da kwance fiye da abubuwan fashewa 14 da ƴan Boko Haram ɗin suka dasa a wurare da dama.

A cewarsa, abubuwan fashewar da aka dasa domin illata farar hula da sojoji, an yi nasarar kwance su a yayin samamen na jami’an soji.

Kovangiya ya ƙara da cewa a tsukin lokacin, sojoji sun samu damar maido da fiye da ƴangudunhijira 987 zuwa yankunansu a Mandaragau da ke ƙaramar hukumar Biu.

Ya ƙara da cewa matakin ya yi daidai da ƙudirin gwamnatin jihar Borno na sake tsugunar da mutanen yankin da kuma dawo da harkokin kasuwanci,” in ji shi.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp