fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Date:

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai a yankin arewa maso gabashin ƙsar sun halaka mayaƙan Boko Haram 17 yayin samamen da suka kai a sassan yankunan jihohin Borno da Adamawa.

Muƙaddashin Darakta a sashen hulɗa da jama’a na rundunar, Kyaptin Reuben Kovangiya, cikin wata sanarwa ya ce mayaƙan sun jima suna cin karensu babu babbaka a ƙananan hukumomin Bama da Konduga da Gwoza da Magumeri da Biu duka a jihar Borno da kuma Michika a jihar Adamawa.

Daily Trust ta ruwaito jami’in na cewa sojojin sun kuma gano tare da kwance fiye da abubuwan fashewa 14 da ƴan Boko Haram ɗin suka dasa a wurare da dama.

A cewarsa, abubuwan fashewar da aka dasa domin illata farar hula da sojoji, an yi nasarar kwance su a yayin samamen na jami’an soji.

Kovangiya ya ƙara da cewa a tsukin lokacin, sojoji sun samu damar maido da fiye da ƴangudunhijira 987 zuwa yankunansu a Mandaragau da ke ƙaramar hukumar Biu.

Ya ƙara da cewa matakin ya yi daidai da ƙudirin gwamnatin jihar Borno na sake tsugunar da mutanen yankin da kuma dawo da harkokin kasuwanci,” in ji shi.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp