fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan bindiga uku a dajin Sambisa

Date:

Rundunar sojin Najeriya da ke aikin yaƙi da ‘yan bindiga a yankin arewa maso gabashin Najeriya ta ce ta kashe ‘yan bindiga uku tare da lalata sansanin ‘yan bindigar a dajin Sambisa.

Cikin wata sanarwar da daraktan yaɗa labaran rundunar sojin ƙasa na Najeriya Onyema Nwachuku ya fitar, ya ce cikin waɗanda sojoin suka kashe har da ɗan ƙunar-baƙin-wake, tare da ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 biyu.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a wani samamen na daban da sojojin suka kai sansanin ‘yan bindigar – da ke yankin Buluwa na ƙaramar hukumar Kukawa – sun kashe wani ɗan bingida guda tare da ƙwato bindiga guda ƙirar AK-47 da harsasai 14 da babur guda ɗaya da kayan abinci da sauran kayayyaki.

A baya-bayan dai matsalar tsaro na ci gaba da addabar wasu sassan arewacin Najeriya, inda a karhsne makon da ya gabata wasu da ake kyautata zato mayaƙan Boko Haram ne suka sace wasu ‘yan gudun hijira fiye da 100 a jihar Borno.

Haka ma a ranar Alhamis ɗin da ta gabata wasu ‘yan bindiga suka sace daliban makarantar furamare da na ƙaramar sakandiren Kuriga a jihar Kaduna.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp