fidelitybank

Sojoji sun kashe ‘yan Bindiga 792 a kasar nan

Date:

Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce ta kashe ƴan bindiga kimanin 792 tsakanin watan Yuli zuwa Satumban da muke ciki.

Cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran hedkwatar, Edward Buba ya fitar, ya ce dakarun tsaron ƙasar, ƙarƙashin rundunar Operation HADIN KAI ta samu nasarar kai hare-hare cikin dajin Sambisa da na Tumbuns a yankin tafkin Chadi, tare da kashe wasu manyan kwamandojin ƴanbindigar.

Sanarwar ta ƙara da cewa hare-haren da sojojin suka kai wa mayaƙan ya rage musu ƙarfi, tare da hana su ƙaddamar da manya-manyan hare-hare.

Edwar Buba ya ci gaba da cewa a lokacin ayyukan soji a waɗanann yankuna tsakanin waɗannan watanni, dakarun ƙasar sun samu nasarar kashe wasu manyan kwamandojin ƴanbingida da suka haɗa da Munzir Arika da Sani Dilla (Ɗan Hausawan Jubillaram) da Ameer Modu da Ɗan Fulani Fari Fari Dungusu da Abu Darda da Bakoura Arina Chiki da Dungusu da Abu Darda da kuma Abu Rijab.

Haka kuma sanarwar ta ce an kama wasu da ake zargi da kasancewa ƴanbidigar kimanin 606 tsakanin waɗannan watanni tare da kuɓutar da mutum 476 da ake garkuwa da su, sannan kuma wasu iyalan ƴanbindigar kimanin 7,283 suka miƙa wuya.

Sanarwar ta kuma ce dakarun sojin sun ƙwato makamai da suka haɗa da bindiga ƙirar AK47 guda 339, da ƙirar gida 58 da ƙananan bindigogi 83 da kuma tarin alburusai.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp