fidelitybank

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Date:

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani kasurgumin dan fashi da makami mai suna Dan Dari Biyar a wani samame da suka kai a unguwar Sabon Birni dake jihar Sokoto.
Majiyoyin soji sun tabbatar da cewa an kashe shugaban ‘yan fashin ne a ranar Alhamis yayin da yake yunkurin karbar kudin fansa daga ‘yan uwan wadanda aka yi garkuwa da su a cikin dajin da ke tsakanin kauyukan Turtsawa, Mazau, da Zango.

An bayyana hakan ne a wani sako da wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Zagazola Makama ya fitar a ranar Asabar ta hanyar X:

“Sojoji sun kashe fitaccen dan ta’addan Dan Dari Biyar a Sabon Birni, jihar Sokoto a lokacin da yake kokarin karbar kudin fansa, ya jagoranci kai hare-hare a wasu al’ummomi da dama.

Rahotanni sun bayyana cewa Dan Dari Biyar ya shahara da zaluntarsa, inda ya rika yin izgili da wadanda abin ya shafa kafin a biya su makudan kudade. An ce yana can ne a cikin dajin Tidibale, kuma yana kai hare-hare a Lalle, Tsamaye, Gidan Sale, da wasu sassan Gwadabawa da Gwaronyo.

Bayanan sirri na sojoji sun alakanta shi da wasu hare-hare na kwanton bauna, samame da kone-kone a shiyyar Sanatan Sakkwato ta Gabas.

Wannan farmakin da sojojin suka gudanar tare da hadin gwiwar jami’an tsaro na cikin gida a karkashin shirin gwamnatin jihar Sokoto na kare al’umma, ya kuma kai ga kwato makamai, alburusai, da na’urorin sadarwa.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp