fidelitybank

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Date:

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani kasurgumin dan fashi da makami mai suna Dan Dari Biyar a wani samame da suka kai a unguwar Sabon Birni dake jihar Sokoto.
Majiyoyin soji sun tabbatar da cewa an kashe shugaban ‘yan fashin ne a ranar Alhamis yayin da yake yunkurin karbar kudin fansa daga ‘yan uwan wadanda aka yi garkuwa da su a cikin dajin da ke tsakanin kauyukan Turtsawa, Mazau, da Zango.

An bayyana hakan ne a wani sako da wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Zagazola Makama ya fitar a ranar Asabar ta hanyar X:

“Sojoji sun kashe fitaccen dan ta’addan Dan Dari Biyar a Sabon Birni, jihar Sokoto a lokacin da yake kokarin karbar kudin fansa, ya jagoranci kai hare-hare a wasu al’ummomi da dama.

Rahotanni sun bayyana cewa Dan Dari Biyar ya shahara da zaluntarsa, inda ya rika yin izgili da wadanda abin ya shafa kafin a biya su makudan kudade. An ce yana can ne a cikin dajin Tidibale, kuma yana kai hare-hare a Lalle, Tsamaye, Gidan Sale, da wasu sassan Gwadabawa da Gwaronyo.

Bayanan sirri na sojoji sun alakanta shi da wasu hare-hare na kwanton bauna, samame da kone-kone a shiyyar Sanatan Sakkwato ta Gabas.

Wannan farmakin da sojojin suka gudanar tare da hadin gwiwar jami’an tsaro na cikin gida a karkashin shirin gwamnatin jihar Sokoto na kare al’umma, ya kuma kai ga kwato makamai, alburusai, da na’urorin sadarwa.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp